Labarai
Jam’iyyar NDC ta musanta labarin ficewar Kwankwaso daga cikin ta

Jam’iyyar NDC ta musanta rahotannin da ake yadawa cewa ɗan takararta na mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2027, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi barazanar ficewa daga jam’iyyar saboda saɓanin da ya taso kan rabon takara a Jihar Kano.
Sakataren Yaɗa Labaran Jam’iyyar NDC, na kasa Osa Director, ya bayyana cewa rahotannin ba gaskiya ba ne.
Director ya bayyana hakan a wata hira da tashar Talabijin ta Arise News, inda ya jaddada cewa Kwankwaso bai taɓa tunanin barin jam’iyyar ba.
Jami’in ya kara dacewa cewa ana samun saɓani a cikin jam’iyya sai dai hakan ba sabon abu ba ne a siyasa, musamman ga jam’iyyar da ke ƙoƙarin kara ƙarfi kafin babban zaɓen 2027.
Ya ce NDC za ta ci gaba da amfani da tattaunawa da sasanci wajen magance matsalolin cikin gida.
You must be logged in to post a comment Login