Connect with us

Labarai

Zanga-zangar rashin tsaro ta shiga rana ta uku a Abuja

Published

on

Masu zanga-zangar, wadanda ke neman gwamnati ta dauki matakan gaggawa wajen inganta tsaro, sun toshe wata gada da ke kan hanyar Karu–Nyanya Expressway, wadda ke hada Jihar Nasarawa da Abuja.

Dauke da alluna masu dauke da sakonni daban-daban tare da rera wakokin nuna rashin amincewa da yadda ake tafiyar da harkokin tsaro, masu zanga-zangar sun bukaci gwamnati ta sauke nauyin da kundin tsarin mulki ya dora mata na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Da farko sun taru ne a kan gadar da ke yankin kafin daga bisani su yi tattaki zuwa Nyanya domin ci gaba da isar da sakonsu.

Zanga-zangar ta haddasa cunkoson ababen hawa mai tsanani a kan hanyar Abuja–Keffi Expressway, lamarin da ya sa matafiya da dama suka makale na tsawon sa’o’i kafin samun damar wucewa.

Masu zanga-zangar sun ce za su ci gaba da matsa lamba har sai an dauki matakan da za su kawo karshen sace-sacen mutane da kashe-kashen da ke addabar al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!