Labarai
Mutuwar Janar Rabe abin kunya ne ga Najeriya – Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce mutuwar tsohon Janar din soja, Major General Abubakar Rabe, a hannun masu garkuwa da mutane na nuna yadda matsalar tsaro ke kara muni a Nijeriya. Ya ce abin takaici ne jami’in da ya sadaukar da rayuwarsa wajen kare kasa ya mutu a hannun ‘yan ta’adda.
Atiku ya kuma danganta lamarin da sabon harin da aka kai a Chibok da kona makarantu, yana cewa hakan ya sake tayar da hankulan al’ummar da har yanzu ba su manta da sace daliban Chibok ba. A cewarsa, hare-haren na nuna cewa ‘yan ta’adda na ci gaba da barazana ga rayuka da kuma ilimi.
Dan takarar shugaban kasa na ADC ya bukaci gwamnatin tarayya ta dauki matakan gaggawa kan matsalar tsaro, yana mai cewa lokaci ya yi da za a wuce alkawura zuwa daukar matakai masu tasiri domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
You must be logged in to post a comment Login