Labarai
Jirgi na biyu na maniyyatan Jigawa zai tashi a yau

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa, ta ce, Jirgi na biyu na maniyyatan jihar zai tashi a yau Talata bayan tashin jirgin farko dauke da maniyyata 480 zuwa kasa mai tsarki a jiya Litinin.
Shugaban hukumar jin dadin alhazai Alhaji Ahmad Umar Labbo ne ya bayyana haka ga wakilinmu Freedom Radio Dutse Aminu Umar Shuwajo.
Haka kuma, shugaban ya jaddada kudirin hukumar bisa sahalewar gwamna Malam Umar Namadi, na tabbatar da bai wa kowane maniyyaci abinci sau uku a kowace rana ciki har da nau’in abincin masu fama da larurar ciwon suga.
Maniyyata 899 ne ake sa ran za su sauke farali bana a jihar ta Jigawa, wadda tini jirin farko ya sauka a birnin Madina tun a jiya Litinin.
You must be logged in to post a comment Login