Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kai tsaye: Cigaba da bikin yaye daliban jami’ar tarayya ta Dutse

Published

on

Note: Ana cigaba da sabinta wannan shafi, ku cigaba da bibiya


Dalibai guda dari 786 ne jami’ar tarayya ta Dutsen jihar Jigawa, ke bikin yayewa a yau.

Rahotanin sun bayyana cewar, daga cikin dalibai dari bakwai da tamanin da shida (786) da ake bikin yayewa, hamsin da biyu (52) sun samu digiri mai matakin daraja ta farko wato First Class.

Kuma wannan shi ne karo na 5 da jami’ar ke bikin yaye dalibai.

Yanzu haka ana dab da kammala wannan biki da dake gudana a babban dakin taro na jami’ar.

A jawabin da ta gabatar, na yau Asabar shugabar jami’ar, Farfesa Fatima Batulu Muktar ta bayyana farin cikinta, tare da godiyar ta ga mahalarta taron inda ta bayyana irin nasarori da jami’ar ta samu musamman a bangaren ilimi da sauran bangarori na ci gaban jami’ar.

Farfesa Batulu Mukhtar ta kuma mika godiyar ta ga abokan hulda musamman gwamnatin jihar Jigawa da sauran dai-daikun al’umma da suka bada gudunmuwa wajen ci gaban jamiar.

Ku kalli hotuna daga wurin taron na yau:

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!