Connect with us

Labarai

Mun ƙara tsaurara tsaro don hana shigowar masu ɗauke da Ebola- FAAN

Published

on

Hukumar Kula da Filayen Jiragen saman Najeriya FAAN, ta ce ta kara tsaurara matakan kariya a dukkan filayen jiragen sama na kasa da kasa sakamakon sake bullar cutar Ebola a wasu sassan tsakiyar Afirka.

Daraktan Hulda da Jama’a da kare hakkin fasinjoji na hukumar, Henry Agbebire, ne ya bayyana hakan inda ya ce, FAAN na aiki kafada da kafada da Ma’aikatar Kula da Lafiya ta Filayen Jiragen Sama da Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta kasa NCDC, domin kara sa ido kan fasinjoji musamman masu shigowa daga yankunan da ake fargabar yaduwar cutar.

A cewar hukumar, ana gudanar da bincike kan fasinjoji domin gano alamomin cutar Ebola, yayin da duk wanda ake zargi zai fuskanci killacewa tare da karin gwaje-gwaje kamar yadda dokokin lafiya na kasa da kasa suka tanada.

Wannan dai na zuwa ne  bayan sake bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo, tare da rahotannin cewa cutar ta bazu zuwa kasar Uganda.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!