Labarai
Kano: Majalisa ta amince da sabbin dokoki 2

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da kudirin dokar Tsare-tsaren Birane da Kula da Ci gaban Gine-gine ta bana, wanda ya soke dokar da ta kafa Hukumar tsara Birane da Raya Kasa ta Jihar Kano, wato KNUPDA.
An zartar da kudirin ne bayan karatu na biyu da na uku a zaman majalisar da aka gudanar a jiya Talata, karkashin jagorancin shugabanta Majalisar, Jibril Ismail Falgore.
Da ya ke ƙarin bayani bayan zaman, shugaban masu rinjaye a majalisar, kuma wakilin Dala, Hon. Lawan Hussaini, ya ce sabuwar dokar ta kafa Hukumar Kula da Yankin Birnin Kano (KAMA) da kuma Hukumar Kula da Tsare-tsare da Gina Muhalli ta Kano (KADCA), wadanda za su gudanar da ayyukansu karkashin Ma’aikatar Filaye da tsarin Birane.
Haka kuma yayin zaman, shugaban majalisar, Jibril Ismail Falgore, ya kaddamar da kwamitin wucin gadi da zai hada gwiwa da Sakataren Gwamnatin Kano domin daidaita ayyukan Ma’aikatar Noma da Ma’aikatar Raya Kiwon Dabbobi.
Ana sa ran kwamitin zai sa ido kan mika dukkan harkokin kiwon dabbobi, kiwon kifi da sauran ayyukan da suka shafi kiwo daga Ma’aikatar Noma zuwa Ma’aikatar Raya Kiwon Dabbobi, kamar yadda Majalisar ta amince.
You must be logged in to post a comment Login