Labarai
Ƙudurin samar da hukumar majalisar masarautu ya tsallake karatu na biyu
Majalisar dokokin jihar Kano ta yi karatu na biyu na kudirin samar hukumar majalisar masarautun jihar.
Hukumar wadda ake sa ran za ta haɗe masarautun Kano baki ɗaya ƙarƙashin jagorancin Sarki Muhammadu Sanusi II, inda zai yi aiki da sarakunan Gaya da Karaye da kuma Rano.
Da ya ke karanta dokar, shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Hussaini Dala, ya bayyana cewa ana zargin zare hannun masarautun gargajiya ya taka rawa wajen taɓarɓarewar harkar tsaro a jihar nan.
Majalisar dokokin ta Kano, ta kuma yi karatu na biyu na dokar samar da wani sashe da zai kula da tsara birane da kuma ci gaban ƙasa.
You must be logged in to post a comment Login