Labarai
Kano: Majalisar Dokoki ta bukaci gwamnati ta zamanantar da asibitin Sabo Bakin Zuwo

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta bukaci Gwamnati da ta zamantar asibitin Sabo Bakin Zuwo da aka fi sa ni da asibitin Jakara.
Ɗan majalisar jiha mai wakiltar Birni, Nabil Sarki Aliyu Daneji ne ya gabatar da ƙudirin a zaman majalisar na jiya Litinin.
Nabill Sarki Aliyu Daneji, ya bayyana cewa asibitin yana bukatar a samar masa da kayan aikin lafiya na zamani, la’akari da muhimmiyar rawar da asibitin ke takawa wajen kula da lafiyar al’ummar ƙaramar hukumar Birni.
A dai zaman majalisar, Wakilin ƙaramar hukumar Ungogo, Sa’ad Aminu Sa’ad, ya gabatar da kudiri inda ya bukaci gwamnati da ta kafa cibiyoyin koyar da sana’o’i a kananan hukumomin Kano 44, baya ga samar da irin su a Tudun Fulani da Zango a ƙaramar hukumarsa ta Ungogo.
Majalisar ta kuma buƙaci kwamitin kula da harkokin kananan hukumomi da masarautu da ya gabatar da rahoton kan matsalar tsaro a Tsanyawa.
You must be logged in to post a comment Login