Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Kano Pillars ta dakatar da daukar sabon mai horar wa

Published

on

Kwana 1 bayan sanar da sunayen mutum 6 da take shirin tantance su ta kuma dauki 1 cikin su, a matsayin sabon mai horas war ta kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta sanar da dakatar da shirin.

A ranar Laraba mai zuwa 1 ga watan Satumba kungiyar dai ta sanar a matsayin ranar da za ta tantance masu horarwawar, kafin daga bisani ta sauya aniyar hakan.

Kano Pillars ta fitar da sunayan masu horarwa 6 da za ta tantance

Rahotanni sun tabbatar da cewar , kungiyar ba ta bayyana dalilan dakatar da tantancewar ba, kamar yadda mai magana da yawun ta Rilwanu Idris Malikawa Garu, ya tabbatar, da dakatarwar.

“An dakatar da tantancewar da kuma shirin daukar, za’a kuma a sake sabon tsari na daukar mai horar war” a cewar Malikawa.

A ranar Lahadi 29 ga Agusta 2021, kungiyar ta Pillars , ta sanar da sunayen mutum shida , da tace za’a tantance su a Talata don samar da sabon mai jagorantar tawagar a Kakar wasannin shekara mai kamawa ta 2021/22.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!