Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Kasar masar ta nada tsohon mai horar da ‘yan wasan Real-Madrid a matsayin sabon jagoran ta

Published

on

Kasar masar ta bayyana tsohon mai horas da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Real-Madrid Carlos Queiroz a matsayin mai horar da ‘yan wasan kasar.

Hakan ya biyo bayan sallamar mai horas da ‘yan wasan na Masar Hossam El-Badry da kasar ta yi sakamakon Kunnan Doki da kasar ta yi a wasan neman tikitin buga gasar cin kofin Duniya da za’a gudanar a kasar Qatar a shekarar 2022.

Qatar 2022: Kasar Masar ta sallami mai horar da ‘yan wasan ta

Kazalika kasar ta bayyana Diaa El-Sayed,  a matsayin mataimakin sa sannan tsohon mai tsaron ragar kasar Essam El-Hadary a matsayin jami’in kungiyar

Carlos Queiroz mai shekaru 68 ya jagoranci kungiyar kwallon kafa ta kasar Portugal zuwa gasar cin kofin Duniya a shekarar 2010 ya kuma horar da ‘yan wasan kasar Iran a shekarar 2014 zuwa 2018.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!