Connect with us

Tsaro

Kasar Turkiyya za ta girke sansanin sojojin ta a Najeriya

Published

on

Najeriya da Turkiyya sun amince da kafa babbar cibiyar horon soji a Najeriya, a wani ɓangare na haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.

 

An cimma yarjejeniyar ce lokacin wata tattaunawar diplomasiyya tsakanin ministocin tsaron ƙasashen biyu a a gefen taron diplomasiyya na 2026.

 

A ƙarƙashin yarjejeniyar dakarun tsaron Najeriya za su riƙa samun horo a fannoni daban-daban na yaƙi da matsalar tsaro kamar ta’addanci da tattatara bayanan sirri da amfani da jirage marasa matuƙa da cire abubuwan fashewa da aka dasa, da kuma atisayen ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD.

 

Najeriya ta jima tana neman haɗin kai da taimakon manyan ƙasashen waje wajen yaƙi da ayyukan ƙungiyoyin ƴanbindiga masu ɗauke da makamai a ƙasar.

 

A watan Fabrairu ne Amurka ta tura dakaru 200 zuwa Najeriya, domin ayyukan horas da sojojin Najeriya da taimaka musu da bayanan sirri.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!