Connect with us

Tsaro

Rundunar Sojin Najeriyar ta lalata maboyar ‘yan bindiga a jihar Borno

Published

on

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta bayyana cewa hare-haren jiragen yaki da ta kai sun lalata maboyar ‘yan ta’adda a yankin Southern Tumbuns da ke Jihar Borno.

 

Rundunar ta ce an gudanar da farmakin ne ranar Juma’a 24-04-2026 da misalin karfe 6:50 na yamma bayan samun sahihan bayanan sirri kan ‘yan tada kayar baya.

Mai magana da yawun rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce jiragen yaki sun fara sintiri inda suka gano wasu ‘yan ta’adda suna bi ta hanyoyin boye zuwa wasu gine-gine da ke karkashin bishiyoyi masu yawa. Bayan tabbatar da su, sai aka kai musu hari da makamai daga sama.

NAF ta ce farmakin ya yi nasara domin an lalata maboyar ‘yan ta’addan, lamarin da zai rage musu karfi a yankin. Rundunar ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da matsa wa ‘yan ta’adda lamba domin kare kasa da al’umma baki daya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!