Tsaro
Sojoji sun kama yan bindiga a jihar Plateau

Rundunar sojin kasar nan sun kama mutane tara da ake zargi mambobin wata ƙungiyar ‘yan bindiga ne a jihar Plateau. Ana zargin su da hannu a kashe-kashe da sauran rikicin kabilanci da ke faruwa a ƙaramar hukumar Riyom.
Ta cikin wani rahoto da shafin Zagazola Makama ya fitar a shafin X ya ce an kama mutanen ne da misalin ƙarfe 1:35 na daren Asabar, bayan da sojoji da ke yankin Ganawuri suka samu bayanin sirri. Bayan kama su, an kuma ƙwato wasu makamai daga hannunsu da suka hada da bindugu.
Wannan mataki na cikin ƙoƙarin da jami’an tsaro ke yi na daƙile rikice-rikice da hare-hare a jihar Plateau.
You must be logged in to post a comment Login