Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kaso 54.6 na yaran Kano ƴan ƙasa da shekaru 5 aka yi wa rijistar haihuwa- UNICEF

Published

on

Asusun tallafa wa ƙananan yara na majalisar dinkin duniya UNICEF, ya ce, kawo yanzu kimanin kaso Hamsin da huɗu da ɗigo shida cikin ɗari na yaran da suke kasa da shekaru biyar aka yi wa rijistar haihuwa a jihar kano duk da irin alfanun da yin rijistar ke da shi.

Shugaban ofishin UNICEF na Kano Rah ma Rihood Mohammed ne ya bayyana hakan, yayin taron tattaunawa da manema labarai kan wayar da kai bisa sabunta tsarin yin rijistar haihuwar ta manhaja watau “DIGITAL”.

Ya ce, akwai buƙatar kafafen yada labarai su kara zaburar da al’umma don ganin kowanne yaro ya mallaki rijistar haihuwa.

“La’akari da mahimmancin da mallakar rijistar haihuwa ke da shi, Domin haka hakki ne akan kowanne iyaye su tabbatar sun sama wa yaran su rijistar haihuwa saboda rayuwarsu ta gaba”

A nasa ɓangaren, Daraktan hukumar kidaya ta Kasa NPC, Alhaji Isma’il ya bayyana cewa, a watan Oktoban da ya gabata hukumar su ta samu damar yi wa yara daga shekaru biyar zuwa ranar haihuwa 225,408,163 a fadin Nijeriya.

Ya ƙara da cewa, hakan ya samo asali ne bisa yadda asusun na UNICEF ya samar Da wadatattun kayan aiki a dukkan kananan hukumomi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!