Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Katin dan kasa : Yadda NIMC ta kama masu yi mata sojan gona a Kano

Published

on

Hukumar samar da katin dankasa wato NIMC, a jihar Kano ta kama wasu mutane dake mata sojin gona.

A shafinta na tiwita hukumar ta ce, mutanen na bayyana kansu a matsayin ma’aikatan ta har ma suna damfarar al’umma akan wai zasu yi musu katin dan kasa.

Hakanan ma NIMC ta ce ta sami wasu daga cikin kayayyakin ta a wasu cibiyoyin kasuwanci a jihar, a lokacin da ta kai samame irin wadannan wurare.

Ta ce tuni ta mika mutanen hannun yansanda domin gudanar da bincike kafin gurfanar dasu a gaban kuliya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!