Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kimiyya

Ko kun san haɗarin kamuwa da lalurar mantuwa?

Published

on

Ƙwararren likitan ƙwaƙwalwa a asibitin Aminu Kano ya ce lalurar mantuwa guda ce daga cikin cututtuka masu saurin hallaka ɗan adam.

Dakta Aminu Shehu na sashin kula da lafiyar ƙwaƙwalwa a asibitin Aminu Kano ne ya sanar da hakan a zantawar sa da Freedom Rdio.

“Lalurar ƙwalƙwalwa na samuwa ne ta hanyar kamuwa da cutar hawan jini, shanyewar barin jiki da kuma sauran cututtukan da kan shafi ƙwaƙwalwa su sanya mata rauni” in ji Dakta Aminu.

Likitan ya ce, a yanzu adadin masu kamuwa da lalurar mantuwa na ƙaruwa, dalilin yadda ake tursasawa ƙwaƙalwa ɗaukan abinda yafi ƙarfin ta.

“Lalurar mantuwa a yanzu ana samun ta akan masu ƙanana da matsakaitan shekaru, saɓanin lokacin baya ana ganin cutar ga waɗanda suka tsufa ko kuma shekarun su suka fara nisa” a cewar likitan.

Alamomin kamuwa da lalurar mantuwa:

“Akan gane alamun kamuwa da lalurar mantuwa ta hanyar rashin tuna wasu abubuwa da suka shuɗe komai muhimmancin su, a wasu lokutan ma masu fama da cutar suna iya manta kan su, ko makusantan su” Dakta Aminu ya faɗa.

Dakta Aminu Shehu ya kuma ce, shaye-shayen miyagun ƙwayoyi na haifar da lalurar, sai dai ana iya dacen warkewa idan da ƙananun shekaru, saɓanin waɗanda shekarun su suka nisa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!