Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kotu ta saka ranar da za ta kawo karshen shari’ar tsohon sarki Muhammadu Sunusi na biyu da gwamnatin Kano

Published

on

Babbar Kotun Tarayya, dake zamanta a Abuja, ta saka ranar 30 ga watan Nuwambar wannan shekara a matsayin ranar da za ta yanke hukuncin karar da tsohon sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi na biyu ya shigar gabanta, na zargin gwamnatin jihar Kano da da take masa hakkin sa.

Mai shari’a Anwuli Chikere, ne ya tsayar da ranar a jiya bayan da lauyoyin bangarorin biyu suka amince da hakan.

Tsohon sarkin na Kano Malam Muhammadu Sunusi na biyu, ya yi karar Sufeton ‘yan sandan kasar nan da shugaban hukumar tsaro na kasa DSS Kan tsareshi da akayi ba bisa ka’ida bah.

Wanda hakan yasa yake karar su kan tauye masa hakkin sa, tare da cusguna masa a lokacin da yake tsare a hannun su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!