Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta yanke wa Ike Ekweremadu, da Mai dakinsa hukuncin ɗaurin shekaru Tara

Published

on

Kotu a kasar Burtaniya ta yankewa tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya Ike Ekweremadu, da mai ɗakinsa, hukuncin ɗaurin shekaru Tara a gidan gyaran hali.

Kotun dai tana tuhumar su da aikata laifin yunkurin safarar sassan jikin dan Adam.

Kotun ta yanke musu hukuncin ne tare da wani likita mai shige musu gaba bayan da suka kai wani matashi Birtaniya daga jihar Lagos.

Sanatan mai shekara 60, da mai ɗakinsa Beatrice ‘yar shekara 56, sun so a cire wa matashin Koda ne da nufin dasa wa ‘yarsu mai suna Sonia ‘yar shekara 25, kamar yadda ma’auratan suka bayyana wa Kotu.

Tun da farko kotu ta samu ma’auratan da likitan mai suna Dakta Obinna Obeta, mai shekara 50, da laifin haɗa baki dashi wajen aikata laifin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!