Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da ƙarar da tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, ya shigar domin ƙalubalantar nasarar tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar ADC.
Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta yanke hukuncin ne bayan lauyan Amaechi, Jibrin Okutepa, ya sanar da kotu cewa ya janye ƙarar saboda ɓangarorin sun sasanta tsakaninsu.
Atiku ya lashe zaɓen fidda gwani na jam’iyyar a watan Mayu da ƙuri’u miliyan 1.846, yayin da Amaechi ya samu ƙuri’u 504,117. Tun bayan bayyana sakamakon, Amaechi ya yi zargin cewa an hana wasu damar kaɗa ƙuri’a kuma an tafka kura-kurai wajen gudanar da zaɓen.
A cikin ƙarar da ya shigar, Amaechi ya nemi kotu ta hana Atiku gabatar da kansa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC a zaɓen 2027, sannan ya nemi a hana Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) amincewa da takararsa.
Sai dai bayan sasanci tsakanin ɓangarorin, kotu ta amince da janye ƙarar tare da share shari’ar daga gabanta. Rahotanni sun nuna cewa tun a watan Yuni ne jam’iyyar ADC ta ayyana Amaechi a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa tare da Atiku domin zaɓen 2027.
You must be logged in to post a comment Login