Connect with us

Labarai

Kotun Sudan ta yanke wa jagoran RSF hukuncin ɗaurin rai da rai

Published

on

Wata kotu a jihar Port Sudan, da ke ƙasar Sudan ta yanke wa jagoran RSF, Mohamed Hamdan Dagalo, da aka fi sani da ”Hemedti”, hukuncin ɗaurin rai da rai.

 

A wata shari’a da aka yi a bayan Hemedti, wanda bai halarci kotun ba, an same shi da laifin aikata kisan ƙare dangi da laifukan yaƙi da laifukan jin ƙai da kuma hare-hare kan fararen hula.

 

Hukuncin kotun da aka yanke ranar Lahadi 12 ga watan Yulin 2026, shi ne mafi girma da aka yi wa jagoran na RSF tun bayan fara yaƙin a 2023.

 

Shari’ar ta mayar da hankali ne kisan da aka yi w gwamnan Yammacin Darfur, Khamis Abbakar, a shekarar 2023.

 

An zargin garkuwa da shi sannan aka kashe shi bayan da ya zargi dakarun RSF da aika kisan ƙare dangi.

 

Hukuncin ya kuma haɗa da wasu manyan jami’ar RSF, ciki har da ƴan’uwan Hemedti, Abdelrahim Dagalo da Algoney Dagalo, duk a bayan idonsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!