Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kuyi dokar da za ta hana jami’an gwamnati zuwa asibitin ketare – Kungiyar likitoci ga majalisa

Published

on

Kungiyar likitoci ta kasa masu neman kwarewar aiki ta bukaci majalisun dokokin tarayyar Najeriya da su samar da wata doka da za ta haramta wa masu rike da madafun iko zuwa asibitocin kasashen waje don kula da lafiyar su.

Shugaban kungiyar likitoci masu neman kwarewar aiki, Dr Uyilawa Okhuaihesuyi shine ya yi wannan kiran ya yi zantawa da manema labarai a Abuja.

Wannan na zuwa ne a lokaci guda da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tafi birnin Lonodn da ke Ingila don kula da lafiyar sa.

‘‘Hakan zai taimaka gaya wajen tursasa jami’an gwamnati da ‘yan siyasa da sauran masu rike da madufin iko da su karkatar da akalarsu wajen kyautata bangaren lafiyar kasar nan’’

‘‘Naira biliyan dari biyar da miliyan saba’in da shida da al’ummar kasar nan ke kashewa a duk shekara wajen ganin likita a kasashen waje, matukar aka yi amfani da wadannan makudan kudade wajen kwaskwarimar asibitoci da sauran cibiyoyin lafiya al’amura da dama za su kyautata’’ inji shugaban kungiyar likitocin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!