Connect with us

Kaduna

Kwamishiniya mai wakiltar jihar Kaduna a Hukumar kidaya ta kasa tayi kira ga alummar jahar kaduna da su fito a kidaya su.

Published

on

Kwamishiniya mai wakiltar jihar Kaduna a Hukumar kidaya ta kasa, Hajiya Sa’adatu Dogon Bauchi tayi kira ga alummar jahar kaduna, da su fito domin a kidaya su.

Ta yi kira ne, a lokacin da ta ziyarci karamar hukumar Sabon Gari, da ke a jahar, inda tace ta hanyar kidayar ne gwamnti za ta iya wadatar da su da ababen more rayuwa.

Ta ja hankalin jama’a game da mahimmacin yin rajista don karbar shaidar yin aure, haihuwa, saki, mutuwa da dai sauran su, wanda ake bayarwa a ofishin Hukumar a duk jihohin kasar nan.

A nasa jawabin, Shugaban karamar Hukumar Malam Jamilu Abubakar Albani  ya  ce, a  shirye suke su bayar da dukkan goyon bayan da ake nema.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!