Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Limamai su rika hudubar da zata kawo hadin kai Sarkin Kano

Published

on

Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bukaci hadin kan limaman juma’a da ke masarautar kan su rika gudanar da huduba da zata kawo hadin kan al’ummar musulmi.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana hakan ne, lokacin da ya ke jawabi ga majalisar limaman juma’a, wadanda suka kai masa ziyarar ta’aziyya ta rasuwar tsohon shugaban majalisar limaman juma’ar Sheikh Fadalu Dan Almajiri, wanda ya rasu a kwanakin baya.

Sarkin na Kano ya ce, hadin kan limaman juma’a, shi ne hadin kan al’ummar Musulmi, wanda hakan zai taimaka gaya, wajen inganta dankon zumunci  tsakanin musulmi.

Da yake jawabi sabon shugaban majalisar limaman juma’a na jihar Kano, Shiekh Nasir Adam, ya ce, suna da tabbacin samun goyon bayan masarautar Kano.

Shima a nasa jawabin, mataimakin sabon shugaban Sheikh Muhammad Sani Nassarawa, cewa ya yi, suna da yakinin samun hadin kan dukkan limaman juma’a na Kano tare da gabatar da huduba kamar yadda Manzon Allah yayi umarni.

Wakilinmu na fadar sarkin Kano Muhammad Harisu Kafar Nassarawa ya rawaito cewa, Sarkin na Kano ya kuma nada dagatai guda uku da suka hada da na Rukusawa, Muhammadu Sabi’u Yahya daga Kumbotso, da Isma’ila Usman na Tokarawa daga Nassarawa, sai kuma Musa Isah na Zangon Bare-bari daga karamar hukumar Unguggo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!