Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Liverpool ta lallasa Arsenal har gida a gasar Firimiya

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Liverpool tayi nasarar doke
Arsenal da ci 2-0 a gasar Firimiya ta kasar Ingila.

Filin wasa na Emirates dai shi ne ya karbi bakuncin fafatawar da ta gudana a ranar Laraba 16 ga Maris din 2022.

A minti na 54 ne dan wasa Diago Jota ya fara zura kwallon farko jim kadan bayan dawowa daga hutun rabin lokaci.

Sai kuma a minti na 62 shima dan wasa Roberto Firmino ya kara kwallo ta biyu da ta tabbatarwa tawagarsa tafiya da maki uku a wasan da ya gudana.

Zuwa yanzu dai Liverpool na mataki na biyu da maki 59 bayan buga wasa 29 a kakar wasannin shekarar 2021/2022.

Inda ita kuma Arsenal ta ke a maki na 4 da maki 51 bayan buga wasanni 27.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!