Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ma’aikatan majalisun tarayya sun yi barazanar dakatar da ayyukansu a majalisar daga ranar Litinin din nan

Published

on

Kungiyar ma’aikatan majalisun tarayya ta yi barazanar dakatar da ayyukan ta a majalisar daga Litinin din nan, kan hakkokin mambobinta da ba’a biya su ba tun shekarar 2019.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi a Abuja dauke da sa hannun wakilan kungiyar su 5.

Ta cikin sanarwar sun ce suna bin bashin naira biliyan 3 da miliyan 1, wanda ya hada da bashin albashin naira biliyan 1 da miliyan 35 da kuma biliyan 1 miliyan 75 da aka ware don yin gyara a tsarin albashi mafi karanci.

A cewarsu, sama da ma’aikata dubu 1,300 ke bin bashin albashi, haka kuma babu wani daga cikin ma’aikatan majalisun dubu 2,345 da ya sami daidaito a mafi karancin albashi, tun lokacin da aka nada su a watan Yunin 2019.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!