Labarai
Mai horar da tawagar Barau FC ya ci zarafin Dan Jaridar Freedom

Mai horar da kungiyar kwallon kafa ta Barau FC, Eugene Agbabe, ya ci mutunci tare da yunkurin dukan dan Jaridar Gidan Rediyo Freedom Kano kana mamba na kungiyar marubuta labaran wasannin ta kasa SWAN reshen jihar Kano , Aminu Halilu Tudun Wada.
Hakan ya biyo bayan da Dan Jaridar ya Tambayi mai horar war tsarin salon amfani da ‘yan wasan sa da ya yi , da ya ce ya kamata ace mai horar war ya samu nasara da kwallaye masu yawa maimakon daya tilo.
Mai horar wa Eugene Agbabe, ya harzuka tare da cewar Dan Jaridar Bai San komai ba a kan kwallo Kuma ba shi da hurumin yi masa tambayar , don haka shi shashasha ne Kuma ya fuskanci daman baya kaunar sa.
A kokarin dai dai ta Lamarin Dan Jaridar Aminu Halilu Tudun Wada, ya cewa mai horar war ya fahimce shi ya Kuma Kwantar da hankalin sa , sai dai mai horar war ya kara harzuka inda ya yunkuro tare da kokarin kai dukka ga Dan Jaridar abinda sauran ‘yan Jaridu da sauran jami’ai a wajen yin hira da ‘yan jaridu suka rike shi, abinda ya sa Dan Jaridar ya bar wajen domin kai Zuciya nesa.
Aminu Halilu Tudun Wada, ya nuna rashin Jin dadin sa inda ya aike da sakon daukar mataki a matsayin kungiyar SWAN, a abinda ya kira cin zarafin sa da mai horar war ya yi a karo na biyu , bayan na farko da ya yi a baya , a wasan da kungiyar ta doke Ikorodu City.
A bangare daya kuma ana dakon abinda kungiyar marubuta labaran wasanni ta SWAN zata aiwatar dangane daLamarin.
You must be logged in to post a comment Login