Connect with us

Labarai

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi Allah wadai da hare-haren Boko Haram

Published

on

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi Allah wadai da hare-haren da ƴan Boko Haram suka kai a garin Darul-Jamal na ƙaramar hukumar Bama da ke  jihar Borno, inda aka kashe akalla Mutane 63, ciki har da fararen hula da sojoji, sannan aka ƙone gidaje da sace mutane.

 

Mai wakiltar Majalisar ta Dinkin Duniya a Najeriya, Mohamed Fall, ya ce lamarin ya sabawa dokokin kare hakkin ɗan Adam, yana kuma kira ga hukumomin Najeriya su kama waɗanda suka shirya harin su gurfanar da su a gaban shari’a tare da gaggauta sakin mutanen da aka sace.

 

Ya kuma jaddada cewa Majalisar za ta ci gaba da tallafawa gwamnati wajen kare fararen hula da dawo da zaman lafiya a yankin arewa maso gabas.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!