Connect with us

Labarai

Majalisar Dattawa ta yi Allah-wadai da sace Dalibai a Oyo

Published

on

Majalisar Dattawan Najeriya ta yi Allah-wadai da sace ɗalibai da malamai da aka yi a jihar Oyo, tana mai bayyana lamarin a matsayin mummunan hari ga makomar ƙasa da kuma ɗan’adam baki ɗaya.

 

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana haka a ranar Talata yayin da majalisar ta koma zaman aiki bayan hutun Sallah. Ya jagoranci sanatoci yin tsayuwar minti ɗaya domin girmama malamai biyu da ɗalibi guda da suka rasa rayukansu sakamakon harin.

 

Akpabio ya ce rashin tsaron da ya shafi makarantu barazana ce ga makomar Najeriya, yana mai jaddada cewa gwamnati da jami’an tsaro na ci gaba da ƙoƙarin ceto waɗanda har yanzu suke hannun masu garkuwa da mutane. Ya kuma miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan da gwamnatin jihar Oyo.

 

Haka kuma, shugaban majalisar ya gargaɗi ‘yan siyasa da masu neman muƙamai da kada su yi amfani da wannan ibtila’i wajen neman farin jini na siyasa, yana mai cewa matsalar tsaro ba ta bambanta jam’iyya, addini ko ƙabila, domin hari ne da ake kai wa Najeriya baki ɗaya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!