Labarai
Majalisar dokoki ta bukaci a kai wa mutanen Sumaila dauki kan ambaliyar Ruwa

Majalissar dokokin jihar Kano, ta karɓi ƙudurin gaggawa na buƙatar gwamnatin jihar da hukumar bada agajin gaggawa SEMA da su kai ɗauki garin Sumaila da Magami a ƙaramar hukumar Sumaila, bisa iftala’in ambaliya da ta sabbaba rushewar gidaje a garuruwan biyu.
A zaman majalisar ƙarƙashin jagorancin shugabanta Jibril Ismail Falgore, wakilin Sumaila, Zubairu Hamza Massu, ne ya gabatar da ƙudurin.
Zubairu Massu ya ce, a halin da ake ciki yanzu mutanen yankin na cikin tashin hankali da suke buƙatar taimakon gaggawa.
A makon da ya gabata majalisar ta kafa kwamiti da zai riƙa lura tare da duba irin wannan iftala’in don magance shi.
You must be logged in to post a comment Login