Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta tsige shugaban masu rinjaye

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta tsige shugaban masu rinjaye na majalisar Alhaji Mohammed Inuwa da ke wakiltar karamar hukumar Doka da Gabasawa.

Hukuncin hakan ya biyo bayan rashin samun magoya baya da yayi daga mambobin zauren majalisar.

Mambobin majalisar 17 na jam’iyyar APC sun kaɗa kuri’ar amincewa da tsige shi daga mukamin shugabancin masu rinjaye na majalisar.

Da yake ganawa da manema labarai jim kadan bayan zaman majalisar, shugaban kwamitin yada labarai Tanimu Musa ya ce, an tsige shi sakamakon rashin samun tabbaci a kan sa.
Sai dai ya ce, za a sanar da sabon shugaban bada jimawa ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!