Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da dokar gwajin jini kafin aure

Published

on

Majalisar Dokokin jahar kano ta amince da dokar yin gwajin cutar kanjamau da ta Sikila da kuma sauran cututtuka kafin yin aure.

Da yake Jawabi akan kafa dokar, Shugaban Majalisar Dokokin jahar kano Alh. Jibril Ismail Falgore ya ce dokar za ta dakile yaduwar cututtuka a tsakanin ma’aurata da yada su ga iyali da al’umma.

Dokar ta ba da damar yin gwajin cututtuka masu hadari da wuyar magani kafin yin aure tare da tanadin hukunci mai tsanani ga duk wanda ya ki biyayya ga dokar.

Mataimakin Akawun Majalisar kuma babban Sakatare Alh. Nasiru Magaji ne ya gabatar da karatu na uku akan dokar kafin amincewa da ita.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!