Labarai
Majalisar Dokokin Kano ta bukaci a dauki matakin gaggawa kan barkewar Diphtheria

Majalisar Dokokin Kano ta bukaci gwamnatin jihar da ta dauki matakin gaggawa kan barkewar cutar Diphtheria cutar mashako, wadda rahotanni suka ce ta hallaka fiye da yara 50 a karamar hukumar Rano.
Dan majalisar mai wakiltar Rano, Ibrahim Muhammad, ya ce cutar ta fi yin kamari a yankunan Rurum da Sabuwar Ƙaura, inda ya bukaci Gwamna Abba Kabir Yusuf, da Kwamishinan Lafiya su kara tura magunguna da ma’aikatan lafiya yankunan.
Da suke goyon bayan ƙudurin, wasu daga cikin ‘yan majalisar sun ce cutar ta bazu zuwa karamar hukumar Kiru, inda ta shafi Kwanar Dangora da Dangora da kuma Yelwa.
Majalisar ta amince da kudirin tare da umartar kwamitinta mai kula da harkokin lafiya da ya tattauna da ma’aikatar lafiya kan aiwatar da dokar kare lafiyar jama’a da kuma samar da agajin gaggawa ga al’ummomin da abun ya shafa.
You must be logged in to post a comment Login