Connect with us

Addini

Majalisar Shari’ar Musulunci ta naɗa Dr Bashir Aliyu a matsayin shugabanta

Published

on

Majalisar Shari’ar Musulunci ta kasa, ta naɗa Sheikh Bashir Aliyu Umar a matsayin shugabanta bayan rasuwar Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.

 

Wata sanarwa da majalisar ta fitar a yau Laraba mai dauke da sa hannun sakataren majalisar Nafiu Baba Ahmed, ta ce, an amince da shuagabancin Dakta Bashir ne kai-tsaye saboda kasancewarsa mataimakin shugabanta.

 

A ranar Litinin ne Sheikh Hadiyyatullah ya rasu a jihar Osun da ke kudancin Najeriya ya na da shekara 81 a duniya.

 

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa, za a sanar da sabon mataimakin shugaban majalisar a nan gaba.

 

Sheikh Dakta Bashir Aliyu Umar sanannen malami ne kuma shi ne babban limamin masallacin Juma’a na Al-Furqan da ke Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!