Connect with us

Manyan Labarai

Malaman Addinin Musulunci sun yabawa Kwamishinan ‘’Yansandan jahar Kano.

Published

on

Zauran malaman jahar Kano sun jinjinawa kwamishinan  ‘’yansanda na jahar Kano AIG Ahmad Iliyasu sakamakon jajircewa da yake yi wajen gudanar da ayyuka da suka hada da samar da tsaro.

Gamayyar malaman da  sanannan likita Farfesa Muhammad Musa Borodo ya jagoranta sun bayyana kwamishinan ‘’yansanda na jahar Kano Ahmad iliyasu a matsayin jajirtacce wajen gudanar da aikin sa  musamman ma samar da tsaro .

Daga nan gamayyar malaman sun taya kwamishinan na ‘’yansanda  Cp Ahmad Iliyasu murnar Karin girma day a samu zuwa matakin mataimakin sufeto na ‘’yan sandan  Najeriya wato AIG.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!