Connect with us

Labarai

Mambobin PDP na Kudu maso Gabas na iya ficewa matukar ta gaza amincewa da Sunday Udeh-Okoye

Published

on

Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ya ce, mambobin jam’iyyar adawa ta  PDP daga yankin Kudu maso Gabashin kasar  na iya ficewa daga  cikin jam’iyyar matukar jam’iyyar ta gaza amincewa da Sunday Udeh-Okoye a matsayin sabon sakataren ƙasa.

 

Gwamna Mbah ya bayyana hakan ne a jiya  Lahadi yayin da yake ganawa da manema labarai bayan wani taron sirri da wasu manyan shugabannin PDP daga Kudu maso Gabas suka yi a fadar gwamnatin jihar Enugu.

 

Cikin manyan shugabannin jam’iyyar da suka halarci taron akwai Gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo, Shugaban Kwamitin Amintattu na PDP, Adolphus Wabara, da Shugaban jam’iyyar a yankin Kudu maso Gabas, Ali Odefa.

 

Sauran sun haɗa da tsohon shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa Okwesilieze Nwodo, da tsohon gwamnan Jihar Ebonyi, Sam Egwu, sai  tsohuwar Ministar Harkokin Mata, Josephine Anenih.

 

Rahotanni sun tabbatar da cewa ana ci gaba da samun rikici a cikin jam’iyyar tsakanin Samuel Anyanwu da Udeh-Okoye kan wanda ya dace da kujerar sakataren ƙasa na jam’iyyar ta  PDP.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!