Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

 Manene dalilan da suka sanya Buhari zuwa kasar Mali

Published

on

A yau Alhamis ne ake sa ran cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bar gida Najeriya don tattaunawa kan batun sasanta rikici tsakanin ‘yan adawa da shugaban kasar Mali.

A dai shekaran jiya ne tsohon shugaban kasar nan Goodluck Jonathan ya yi ganawar sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari bayan da kungiyar ECOWAS ta nada shi ya jagoranci kwamtin sasanta rikici tsakanin shugaban kasar Mali Boubacar Keita da ‘yan adawa.

Daga cikin shugabanin kasashen Afrika ta yamma da ake kyautata zaton za su halaci taron akwai Alassane Outtara na Cote d’Ivoire da Nana Akufo Addo Ghana da na Senegal Macky Sall

Wannan na kunshe cikin sanarwar da mashawarcin shugaban kasa kan kafafan yada labarai Femi Adesina ya sanyawa hannu wacce jaridar Punch ta wallafa a jiya.

Shugaban jamhuriyyar Niger Issoufou Mahamadou ya amince su hado a Bamako babban birnin kasar don tattuna batun sasatan rikicin siyasa da ya kunnu kai a kasar ta Mali.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!