Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Matashin da ya mayar da wayar dubu 60 da ya tsinta a Kano

Published

on

Wani matashi mai suna Abdurrahman Abdulkarim ya mayar da wayar salula da ya tsinta ta kimanin Naira dubu sittin.

Matashin ɗan unguwar Fagge ne, kuma ɗalibi a makarantar Sakandire ta Ƙofar Nassarawa.

Abdurrahman ya shaida wa Freedom Radio cewa, ya tsinci wayar ne a baburin adaidata sahu.

Daga nan ne kuma suka riƙa waya da mai wayar har ya tafi ya same shi domin mayar masa da wayarsa.

Ya ce “Idan na riƙe wayar ba abin da za ta ƙaramin domin ba tawa ba ce, shi yasa na ga bani da zaɓi fa ce na mayar masa”.

“A baya ma na taɓa tsintar waya ta wani dattijo, kuma na mayar masa”.

Shi ma a nasa ɓangaren mamallakin wannan waya Alhaji Bala Muhammad Nasir, ya yi wa matashin godiya tare da ba shi tukuici.

Ya ce “Na yi farin ciki matuƙa da irin nagartar da wannan matashi ya nuna, tabbas abin a yaba masa ne”.

Babban Kwamandan hukumar Hisbah na jihar Kano, Ustaz Muhammad Haruna Ibn Sina ya jinjinawa iyayen wannan matashi.

Ya ce, babu shakka iyayen sun yi abin ƙwarai wajen tarbiyyar ƴaƴansu.

Ibn Sina ya yi kira ga sauran jama’a da su yi koyi da irin kyawun halin da Abdurrahman ya nuna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!