Labarai
MDD ta koka kan yadda yan Najeriya ke wahalar samun takin zamani

Mataimakiyar sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Amina Muhammed ta nemi gwamnatin kasar nan ta samar da sabbin tare-tsare da za su baiwa manoman ƙasar damar samun takin zamani.
Amina ta bayyana haka ne yayin tattaunawarta da jaridar TheCable da ke Najeriya, a birnin Washignton DC na Amurka, yayin da aka mata tambaya kan yadda za a bunkasa samar da abinci a kasar nan.
Ta ce “Yadda Najeriya ke fitar da takinta na taimakawa wajen habbaka tattalin arzikinta sai dai kuma manoma a cikin gida ba sa iya saya saboda tsada”.
Ta kuma bayar da shawarar gwamnati ya kamata ta haɗa hannu da masu masana’antu na cikin gida domin samar da takin ga manoman da ke cikin gida.
You must be logged in to post a comment Login