Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ministan shari’a ya amince da halartar zaman kwamitin bincike na majalisar wakilai

Published

on

Ministan shari’a na Nijeriya Abubakar Malami SAN, ya amince da halartar zaman kwamitin bincike na majalisar wakilai kan yadda aka sayar da ganga miliyan 48 ta danyen man fetur ba bisa ka’ida ba a shekarar 2015.

Shugaban kwamaitin binciken Mark Gbillah, ne ya sanar da hakan ga manema labarai jiya Alhamis a birnin tarayya Abuja.

Ya ce, Ministan zai bayyana a gaban kwamitin a ranar 27 ga wannan watan da muke ciki na Afirilu.

Mark Gbillah ya kara da cewa kwamitin ya gano yadda Abubakar Malami ya karbi wasu kudade daga kasashen ketare ba bisa tsarin nan na bayar da lada ga masu kwarmata bayanan sirri game da cin hanci da rashawa ba.

Ya kara da cewa bincikensu ya gano cewa ministar kudi Zainab Ahmad ce ta sahale biyan kudin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!