Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar Soji ta bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin samar da tsaro

Published

on

Babban hafsan rundunar sojin kasa ta kasar nan Laftanal Janar Christopher Musa ya bai wa al’ummar Najeriya tabbacin cewa dakarun rundunar soji za su yi duk mai yiwuwa wajen dakile duk wata barazanar rashin tsaron dake faruwa a fadin kasar nan.

Laftanal Janar Christopher Musa, ya bayyana hakan ne a Talatar makon nan, lokacin da ya ke gabatar da jawabi ga dakarun Operation Hadarin Daji a jihar Sokoto.

Haka kuma, ya jinjina wa dakarun rundunar sojin kasa bisa irin namijin kokarin da suke yi na yaki da ayyukan ta’addanci a fadin Nijeriya musamman yadda suke nuna kwarewa a bakin aikin.

Ya kara da cewa rundunar tana sane da irin yadda dakarun nata suke rasa rayukansu da kuma yadda wasu suke samun munanan raunuka harma da irin yadda iyalansu suke jure rashinsu duka a yakin da suke yi da ayyukan ‘yan ta’adda a sassa daban – daban a Najeriya.

Laftanal Janar Christopher Musa, ya kuma bukaci dakarun da su yi hakuri kuma kada su gajiya, domin za su magance duk wasu matsalolin da kasar nan take fuskanta musamman yakin da suke yi da masu garkuwa da mutane da sauran ayyukan ‘yan ta’adda.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!