Connect with us

Labarai

Mutane 21 sun mutu a gobarar da ta tashi a Delhi

Published

on

Aƙalla mutum 21 sun mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata bayan da gobara ta tashi a wani babban gini mai tsawo a Delhi.

 

Marasa lafiya da ƴan uwansu da ke karɓar kulawa a wani asibiti mai zaman kansa da ke kusa ne ke zama a ginin da gobarar ta tashi.

 

Rahotanni sun bayyana cewa da dama daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su ƴan ƙasashen waje ne, kamar Najeriya, Mozambique da Bangladesh da Laberiya, waɗanda suka je India domin neman lafiya, ko kuma suka rako ƴan uwansu da ba su da lafiya.

 

Shaidu sun bayyana cewa wutar ta yi ta bazuwa cikin sauri, lamarin da ya sa waɗanda ke sama kasa tserewa.

 

Wakilin BBC ya ruwaito cewa ƴan sanda sun ce an kashe gobarar, sai dai har zuwa fitar da wani rahoto ba a san musababin tashinta ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!