Connect with us

Labarai

Ku haɗa kai wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro a Najeriya – Abdulsalami Abubakar

Published

on

Tsohon Shugaban Ƙasa na mulkin soja, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya, ya bukaci ‘yan Najeriya da su haɗa kai domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta addabi ƙasar nan. 

Janar Abdulsalami Abubakar ya ce yaƙi da ta’addanci da sauran laifuffuka ba aikin jami’an tsaro kaɗai ba ne, kowa yana da rawar da zai taka.

A cikin saƙon da ya fitar yayin bikin cika shekaru 84 da haihuwarsa, Abdulsalami ya nuna damuwa kan yadda rashin tsaro ke ƙara ta’azzara, inda ya ce mutuwar Manjo Janar Abubakar Rabe da sauran waɗanda suka rasa rayukansu na nuna buƙatar haɗin kai cikin gaggawa.

Ya yi gargadin cewa siyasantar da batutuwan tsaro da kuma yaɗa labaran ƙarya a kafafen sada zumunta na ƙara ba ƙungiyoyin ta’adda ƙarfi. 

Saboda haka, ya buƙaci ‘yan Najeriya su ajiye bambance-bambancen ƙabila, addini da siyasa, su haɗa kai da gwamnati da jami’an tsaro domin dawo da zaman lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!