Labarai
Janar Rabe mai ritaya ya rasu a hannun ‘yanbindiga bayan garkuwa da shi

Tsohon mai magana da yawun rundunar tsaron Najeriya, Manjo Janar Abubakar Rabe ya rasu a hannun ’yan bindiga a jihar Katsina.
Gwamnatin Katsina ce ta tabbatar da hakan a wata sanarwa da kwamishinan tsaron cikin gida ya fitar, inda ya ce tsohon hafsan ya rasu ne sakamakon ta’azzarar ciwon suga da hawan jini yayin da yake tsare a hannun masu garkuwa da mutane.
Sanarwar ta bayyana cewa duk da kokarin da gwamnatin jihar tare da jami’an tsaro suka yi na ganin an kubutar da shi cikin koshin lafiya, lamarin ya kare da wannan mummunan sakamako.
Mutuwar tasa ta jefa iyalansa da al’ummar jihar Katsina da ma kasa baki ɗaya cikin alhini.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya mika sakon ta’aziyya ga iyalan marigayin tare da bayyana lamarin a matsayin babbar asara.
Ya ce wannan wata alama ce dake nuna bukatar kara hada kai domin tinkarar matsalar tsaro da ke addabar al’umma.
A kwanaki baya ne dai yanbindida suka sace Jamar Rabe da matarsa a Katsina, inda suka nuna su a bidiyo suna kira ga hukumomin Najeriya su ceto su.
You must be logged in to post a comment Login