Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NAFDAC ta kama jabun magunguna a Kano

Published

on

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa, NAFDAC a nan Kano ta kai wani sumame karamar hukumar Bichi tare da kama wasu jabun magunguna da allurai na kimanin miliyan sha biyar.

Tun da fari dai wani mutum mai suna Muhammad Jamilu Sani Wanda ke hada magunguna da allurai na dabbobi a wani gida.

Shugaban hukumar Shaba Muhammad shi ne ya jagoranci sumamen ya bayyanawa wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail cewar sama da watanni 6 suna neman inda ake hada wannnan magani sai yanzu suka samu nasarar damke wannan mutum.

Shaba Muhammad ya kuma bayyana cewar zasu kai maganin da alluran dakin gwaji domin gano ko suna da illa ga lafiyar dabbobi, ya kuma ce cewar da zarar sun kammala bincike zasu gurfanar da jamilun a gaban kotu dan ya girbi abin da ya shuka

Shima Wanda aka zargin Muhammad jamilu ya bayyana cewar ya na da shaidar kammala karatu na babbar difiloma wanda yaje kwalejin Audu bako ya koyo ilimin harhada magungunan dabbobi.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito cewa tuni dai hukumar tayi awon gaba da magungunan da alluran don fadada bincike a kan su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!