Connect with us

Labarai

Najeriya na cikin ƙasashen da ake kai hari kan cibiyoyin kiwon lafiya – WHO

Published

on

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta ce Najeriya na cikin ƙasashen da aka samu rahotannin kai hare-hare kan jami’an lafiya da cibiyoyin kiwon lafiya.

 

WHO ta ce an tabbatar da sama da hare-hare 10,000 kan harkokin lafiya tun daga shekarar 2018 zuwa yanzu, a ƙasashe da yankuna 29.

 

Hare-haren sun yi sanadin mutuwar kusan mutum 5,700 tare da jikkata wasu 8,500, amma WHO ta ce kawo yanzu ba a gurfanar da kowa a gaban hukuma kan waɗannan hare-hare ba.

 

Altaf Musani, daraktan sashen agaji da kula da bala’o’i na WHO, ya bayyana alaluman a wani taron manema labarai a Geneva.

 

Ya ce cibiyoyin lafiya da tsarin kiwon lafiya na ƙarƙashin kariyar dokokin ƙasa da ƙasa, musamman dokokin jinƙai da haƙƙin ɗan Adam da yarjejeniyar Geneva ta tanada.

 

Sai dai ya ce duk da sama da hare-hare 10,000 da WHO ta tabbatar, “babu ko guda ɗaya da ya shiga tsarin da zai kai ga hukunta masu aikata su.”

 

A cewar rahoton a bana kaɗai, hukumar lafiyar ta WHO  ta tabbatar da hare-hare 914, waɗanda suka kashe mutum 911 tare da jikkata 1,486.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!