Labarai
Najeriya ta tura sojoji zuwa Gambia domin wanzar da zaman lafiya

Rundunar Sojin Sama ta kasar nan ta sanar da tura sabbin sojoji 198 zuwa ƙasar Gambia domin ci gaba da aikin wanzar da zaman lafiya ƙarƙashin tawagar ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen Yammacin Afirka ECOWAS.
A cewar rundunar, an yi jigilar sojojin ne ta jirgin dakon kaya na C-130H, inda aka kai dakarun rundunar domin su maye gurbin waɗanda ke cikin rundunar NIGCOY 10 ECOMIG, bayan sun kammala wa’adin aikinsu.
Rundunar ta bayyana cewa an gudanar da sauya dakarun ne a zagaye biyu tsakanin 26 da 30 ga Mayun 2026, tare da jigilar kayan aikin soji da kayayyakin amfanin mutanen da aka tura domin tabbatar da cewa an mika ragamar aikin cikin tsari ba tare da tangarɗa ba.
NAF ta ce nasarar gudanar da wannan aiki ta nuna irin ƙarfin da rundunar ke da shi wajen jigilar dakaru cikin gaggawa zuwa ƙasashen waje domin tallafa wa ayyukan wanzar da zaman lafiya da tabbatar da tsaro a yankin.
You must be logged in to post a comment Login