Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

NECO ta fitar da sakamakon jarrabawar 2021

Published

on

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta ƙasa NECO ta sanar da cewa ta fitar da sakamakon jarrabawar ɗaliban shekarar 2021.

Shugaban hukumar Farfesa Dantali Wushishi ne ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai a Minnan jihar Neja.

Farfesa Dantali Wushishi ya ce, cikin ɗalibai miliyan ɗaya da dubu ɗari biyu da talatin da uku da suka yi rijistar rubuta jarrabawar a bana, ɗalibai miliyan ɗaya da dubu ashirin da shida da ɗari shida da talatin da ɗaya ne kaɗai suka rubuta jarrabawar.

A cewar sa, ɗalibai dubu ɗari tara da da arba’in da biyar, da ɗari takwas da hamsin da uku ne kawai suka samu Credit 5 ciki har da lissafi da turanci, yayin da ɗalibai dubu ɗari da casa’in da huɗu, da dari biyu da casa’in da ɗaya ne ba su samu lissafi da turanci ba.

Farfesa Dantali Wushishi ya ce, wannan ya nuna cewa, kaso sama da saba’in da ɗaya ne suka samu nasara cikin ɗari, kuma ya nuna cewa a bara an fi samun nasara da kaso sama da 73 cikin ɗari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!