Connect with us

Labarai

Neja: Yan Sanda sun kama mutane 5 da ake zargi da haɗa kai wajen aikata fashi

Published

on

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja ta kama mutane 5 da ake zargi da haɗa baki wajen aikata fashi da makami a wasu yankunan Minna, tare da kwato ƙaramar bindiga ƙirar Barretta guda ɗaya da harsasai biyu.

 

Hakan na cikin sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, SP Wasiu Abiodun, ya fitar aka rabawa manema labarai.

 

Ya ce, lamarin ya faru ne ranar 11 ga Agusta 2026, bayan wasu masu fashi da makami sun shiga gidaje a yankin Sauka Kahuta da ke Minna, inda suka sace kwamfutoci, wayoyi, babura da sauran kayayyaki.

 

Sanarwar ta ce, binciken ’yan sandan ya kai ga kama jagoran ƙungiyar, wanda daga bisani ya taimaka wajen kama sauran mutum uku da ake zargi da hannu a hare haren fashi da aka yi a wasu yankunan Minna.

 

Rundunar ta ce daga baya ta kama mutum na biyar da ake zargi da ajiye musu bindiga, inda aka kwato bindigar Barretta mai harsasai 2. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!