Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Norwich City ta sallami Daniel Farke bayan samun nasarar wasa a Firimiya

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Norwich City dake kasar Ingila ta sallami mai horar da ‘yan wasan ta Daniel Farke.

Norwich dai ta sallami mai horarwar ne a ranar Asabar 6 ga watan Nuwambar 2021.

Sallamar nasa na zuwa ne awanni kadan bayan samun nasara da ya yi akan Brentford a gasar Firimiyar kasar ta Ingila da ci 2-1.

Kuma itace nasara ta farko daya samu a gasar ta shekarar 2021/2022.

Yanzu haka dai Norwich itace ta 20 kuma ta karshe a gasar Firimiyar ta Ingila da maki 5 cikin wasanni 10 da mai horarwar ya jagoranci kungiyar a bana.

Daniel Farke, dan asalin kasar Jamus, ya fara jagorantar horar da ‘yan wasan kungiyar ta Norwich City a shekarar 2017, inda ya jagoranci wasanni 208 ya kuma samu nasara a wasanni 87.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!